Duniya ina zaki damu : Wani matashi yayiwa dan’uwansa yankan rago.
Wani matashi da aka bayyana sunansa da junaidu ahmadu yaro, mazaunin karamar hukumar katsina ala dake jihar benue, ya cakawa dan’uwansa wuka a sanadin fadan cultism a wani otal.
Bayan ya aikata laifin kisan yayi yunkurin guduwa sai jami’an yan sanda suka kamashi a rice mill house quarters dake karamar hukumar katsina ala cikim jihar benue.
- Dalilin da yasa amare basa cin kazar da ango ke kawowa a daren farko
- Wani kare ya mutu har lahira bayan ya shinshini dan kampai
- Rahma Sadau: Yadda na tsallake rijiya da baya a harin jirgin kasar kaduna
- Kalli yadda samari su ke gudun wata budurwa saboda tsawon ta
Marigayin da aka kashe mai suna, Nurain dan bala, yataso ne daga jihar calabar zuwa katsina ala domin halartar bikin murnar zagayowar watan da aka haifi fiyayyen halitta, annabi muhammad s a w.
Jaridar DAILY NEWS HAUSA ta ruwaito cewa ahi marigayin da aka kashe, Ya sauka a keke napep kenan junaidu ya daba masa wuka, wanda hakan yayi sanadiyyar mutuwarsa.
Zuwa yanzu dai matashin yana ofishin yan sanda yana amsa tambayoyi, a halin da ake ciki ya lissafo mutane kimanin goma wadanda aka aikata fadan dasu,dukkansu yan sanda sun bisu sun kamasu.








